Anyi jana’izar Mutum 80 Da Harin Jirgin Sojojin Najeriya Ya Kashe A Kaduna
Ya kara da cewa akwai mutum 66 suka raunata da aka kai su asibitin Barau Dikko da ke garin Kaduna domin samun kulawa.
Wannan ba shi ne karon farko da muke Mauludi a garin ba da daddare, domin ko a makon jiya mun yi Maulidi kuma babu abin da ya faru, sai a wannan karon,” in ji shi.
Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta dauki alhakin harin, wanda ta ce jirginta ne ya kai harin kan fararen hula bisa kuskure a lokacin da yake sintirin yaki da ’yan ta’adda.
Yankin Tudun Biri dai na kusa ne hanyar Birnin Gwari, a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya da ke fama da matsalar hare-haren da ke wa mutane kisan gilla da kuma garkuwa da su domin karbar kudin fansa.