Kaf ƴan matan kannywood babu mai kwana gidan iyayenta – Murja kunya

“Duk yan matan kannywood a fadamin mace daya ta take zama gidan iyayenta , wanda kun kayi imani cikinmu gidan iyayenta take zama, duk wanda take da iyaye wanda suke tsaye duk kallon tausai suke mana idan baku sani ba yau ku sani ba yau.

A fadi mace daya tun daga murja wanda take zama a gidan iyayenta dindindin idan ma tana zama gidan iyayen ta, a kawomin mace daya ta ke jin maganar iyayenta, maganar jin iyaye ina nufin wadda zatayi wanka tayi kwana tace zataje daukar fim sati daya suce bazata je ba fasa a kawomin ita.

Idan ma akwai wadda take zama gidan iyayenta, iyayenta ne ke juyata, billahilazi a’illahah illah huwa na rantse da Allah duk mudinan da kunka ganinmu muke ciyarda iyayenmu , muke rike da gidanmu wannan shine gaskiya iyayen mu suke jin tsoro su tunkare mu su gayamana gaskiya ,kar wadda ta kirani a waya tayimin wani shirme – inji murja kunya

Murja kunya tace ita yanzu tana gefe ba tiktok ne a gabata ba tunda bata shiga harka uban kowa ba babu ruwana da shi, murja tayi maganganu masu zafi sosai da zaku iya saurara kuji a cikin bidiyon.

Post a Comment (0)
Previous Post Next Post